News

Gaskiyar Magana Akan Cire Rubutun Ajami Na Kuƌin Najeriya 

Ana dab da canza fasalin kudin Najeriya kamar yadda babban bankin kasa yasanar wa yan kasa cikin wannan mako day a gabata.

Canza fasalin za’ayishi ne a kan Naira 200, 500 da kuma 1,000 kamar yadda labarin ya fito daga bankin Najeriya wato central bank of Nigeria (CBN).

Saiadai bayan ‘yan kasa sun sami wannan labara na canza fasali sai kafafen sada zumunta na wannan zamani ya cika da cece kuce inda wasu ke fadar a cewa yana daya daga cikin canjin inda za’a share rubutun ajami dake jikin kudin, wanda wannan takaddama ke faman yawo kusufa kusufa.

Siadai a karshe tsohon sarkin kano kuma tsohon gwamnan babban banki wato Sunusi Lamido Sunusi ya wanke wannan tantama inda ya fayyace yadda abin yake a fili.

Tshohon gwmanan yace:

“yaji mutane nata yada jita-jita wai za’a cire ajami na jikin kudin Najeriya inda har wasu malamai suka fara mayar da martini wanda hakan ba gaskiya bane domin na kira gwmanan banki mista Emefele inda yafadamin cewa wannan Magana bah aka take ba, wasu ne kawai ke yada jita-jita”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button